Jam’iyyar NDC na gudanar da babban taronta na ƙasa

Jam’iyyar hamayyar ta NDC a Najeriya na gudanar da babban taronta na ƙasa domin zaɓen sabbin shugabanninta.

Matakin na zuwa ne mako guda bayan da manyan jiga-jigan siyasar ƙasar biyu, Peter Obi da Kwankwaso suka sanar da komawa cikinta.

Ɗaruruwan magoya bayan jam’iyyar ne suka taru a harabar wurin gudanar da taron a Abuja.

Akwai bayanai masu ƙarfi da ake yaɗawa cewa Peter Obi da Kwankwaso ne jam’iyyar za ta bai wa takarar shugaban ƙasar a jam’iyyar.

Post masu alaƙa

Najeriya ta ƙarfafa ƙawancen tsaronta da Amurka

EFCC ta ayyana neman Sadiya Farouq ruwa a jallo

Rundunar ƴan sandan Kano tare haɗin gwiwar sojoji sun ƙwato Shanu 67 daga hannun ɓarayi