Jam’iyyar hamayyar ta NDC a Najeriya na gudanar da babban taronta na ƙasa domin zaɓen sabbin shugabanninta.
Matakin na zuwa ne mako guda bayan da manyan jiga-jigan siyasar ƙasar biyu, Peter Obi da Kwankwaso suka sanar da komawa cikinta.
Ɗaruruwan magoya bayan jam’iyyar ne suka taru a harabar wurin gudanar da taron a Abuja.
Akwai bayanai masu ƙarfi da ake yaɗawa cewa Peter Obi da Kwankwaso ne jam’iyyar za ta bai wa takarar shugaban ƙasar a jam’iyyar.