Tsohon mataimakin gwamnan Kano Aminu Abdussalam ya fice daga NNPP
A hukumance, tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdulsalam Gwarzo, ya fice daga jam’iyyar NNPP. Gwarzo ya sanar da ficewar tasa ne cikin wata wasika da ya aike wa shugaban jam’iyyar NNPP na mazaɓarsa ta Gwarzo, inda ya bayyana cewa ya dauki wannan mataki ne sakamakon sabbin sauye-sauyen siyasa da ke faruwa a jihar Kano. […]