Home » Tinubu Ya Yi Farin Ciki Da Ricikin Jam’iyun Adawa

Tinubu Ya Yi Farin Ciki Da Ricikin Jam’iyun Adawa

by Mujahid Wada Guringawa
0 comment

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ce yana farin ciki da halin rikici da jam’iyyun adawa da dama na ƙasar ke ciki.

Shugaban ya bayyana haka ne a lokacin jawabin da ya yi na ranar tunawa da dimokuraɗiyya a zauren majalisar dokokin ƙasar da ke Abuja, yau Alhamis.

“Ina jin daɗin ganin jam’iyyun adawa a tagayyare,” kamar yadda shugaban ƙasar ya bayyana a jawabinsa na ranar dimokuraɗiyya.

Tinubu ya ce “ba zan ce ina so na ga kun gyaru ba, ina ma jin dadin ganin ku a haka.

Hakan na zuwa ne yayin da jam’iyyar APC mai mulkin ƙasar ke ci gaba da karɓar ƴan siyasa masu sauya sheƙa daga jam’iyyun adawa zuwa cikinta.

Tinubu ya ce jam’iyyar APC ba za ta hana kowa shiga cikinta ba domin yin hakan tauye hakkin al’umma ne.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?