Home » Tsohon shugaban kasa, Buhari, ya sauya wurin zama saboda yawan jama’a masu kai masa ziyara

Tsohon shugaban kasa, Buhari, ya sauya wurin zama saboda yawan jama’a masu kai masa ziyara

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Tsohon shugaban kasa, Buhari, ya sauya wurin zama saboda yawan jama'a masu kai masa ziyara

Tsohon shugaban ƙasa Muhammad Buhari ya bar mahaifarsa Daura da ke jihar Katsina inda ya tare tun  bayan saukarsa daga mulki.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da tsohon maitaimaka masa akan harkokin ƴaɗa labarai Malam  Garba Shehu ya wallafa a shafinsa na Twitter.

Sai dai malam Garba  shehu bai bayyana inda tsohon shugban ya komada zama ba.

Malam Garba Shehu ya ce, dattijon baya samun yadda yake so a garin na Daura, duk da ya bar kan mulki, mutane su na yawan kai masa ziyara, saboda haka ya sake lulawa zuwa wani wuri mai nisa domin ya yi rayuwa cikin sukuni.

Ya ce, Buhari ya koka da irin cinci-rindon da masu ziyara suke yi masa dare da rana a lokacin da yake kokarin samun hutu.

A cikin jawabin nasa malam Garba Shehu ya ce, dama  Buhari ya tafi Daura ne da nufin ya samu irin rayuwar da yake so ta rashin hayaniya, amma sai ya fahimci ba haka lamarin yake ba.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?