Home » Yemen: Mutane 85 Sun Rasu, 320 Sun Jikkata Yayin Karɓar Tallafin Kuɗi

Yemen: Mutane 85 Sun Rasu, 320 Sun Jikkata Yayin Karɓar Tallafin Kuɗi

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Akalla rayukan mutane 85 sun salwanta ciki har da mata da yara yayin da wasu mutanen fiye da 320 suka ji munanan raunika bayan aukuwar wani turmutsitsi a birnin Sanaa da ke karkashin ‘yan tawayen Houthis na kasar Yemen.


Turmutsitsin ya auku ne a yayin da ake rabon taimako na kudade ga marasa karfi a wata makaranta da ke wata Unguwa da ake kira Bab el Yemen kamar yadda wani jami’in gidan asibitin dake karkashi ‘yan tawayen da ke da iko da yankin ya tabbatar.


Har kawo yanzu dai hukumomi ba su yi bayani ba kan musabbabin tirmimutsitsin mafi muni da aka samu a tarihin kasar, kana kuma ba su fitar da alkaluman wadanda lamarin ya ritsa da su ba.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?