• Home  
  • Za mu ɓullo da sabon salon yaƙi da talauci da ta’addanci ~ Shugaba Tinubu
- Labarai

Za mu ɓullo da sabon salon yaƙi da talauci da ta’addanci ~ Shugaba Tinubu

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ce gwamnatinsa tana aiwatar da shirye-shirye da manufofin da za su bai wa ‘yan kasa damar yaki da kalubalen talauci da aikata laifuka da ta’addanci.

Za mu ɓullo da sabon salon yaƙi da talauci da ta'addanci ~ Shugaba Tinubu

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ce gwamnatinsa tana aiwatar da shirye-shirye da manufofin da za su bai wa ‘yan kasa damar yaki da kalubalen talauci da aikata laifuka da ta’addanci.

Shugaban ya ce shirye-shiryen da gwamnatinsa za ta bullo da su wani sabon salo ne na samar da tsaro.

A cewarsa, shirin zai kasance ne ta hanyar jajircewa wajen tinkarar kalubalen tsaro da ke yin barazana ga wannan kasa da ma yankin yammacin Afirka.Shugaba Tinubu ya kuma umarci duka shugabannin tsaro da su hada kai a kokarin da suke yi na kare martabar duka yankunan kasar nan.

Duka wadannan bayanai da shugaba Tinubu ya yi suna kunshe ne a cikin jawabinsa da mataimakinsa Kashim Shettima ya karanta lokacin da ya wakilce shi a wajen bikin kaddamar da horas da dalibai 70 a makarantar sojoji ta Nijeriya (NDA) dake jihar Kaduna a ranar Asabar.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000