• Home  
  • Ƙungiyar Ƙwadago Ta Umarci Mambobin Ta Da Su Shiga Yajin Aiki
- Babban Labari - Labarai

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Umarci Mambobin Ta Da Su Shiga Yajin Aiki

NLC ta ce za’a fara yajin aikin ne daga ranar 1 ga watan Disamba har sai sanda gwamnati da ɗauki matakin fara biyan sabon mafi ƙarancin albashin. NLC ta bayyana rashin biyan sabon albashin a matsayin yin karan tsaye ga doka da kuma jefa miliyoyin yan Najeriya cikin wani hali. Majalisar Zartarwar NLC ta ƙara […]

NLC ta ce za’a fara yajin aikin ne daga ranar 1 ga watan Disamba har sai sanda gwamnati da ɗauki matakin fara biyan sabon mafi ƙarancin albashin.

NLC ta bayyana rashin biyan sabon albashin a matsayin yin karan tsaye ga doka da kuma jefa miliyoyin yan Najeriya cikin wani hali.

Majalisar Zartarwar NLC ta ƙara da cewa akwai yaudara da kuma bautar da ma’aikata, yanda wasu gwamnonin suka ƙi fara biyan sabon mafi ƙarancin albashin.

Wannan umarnin na fitowa ne bayan da kungiyar ta gudanar da taron Majalisar zartaswa a ƙarshen makon nan, in da ta bayyana takaicin ta ga yadda gwamnonin ƙasar ke take doka.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai