Ƴan bindiga sun sace basarake da matarsa a jihar Kwara

Wasu da ake zargin yan bindiga sun kai farmaki fadar wani basarake, tare da sace shi da matarsa a ƙauyen Olayinka, da ke ƙaramar hukumar Ifelodun a Jihar Kwara.

Rahoton ya nuna cewa maharan sun kai farmaki fadar Oba Salman Aweda da misalin ƙarfe 1:40 na dare ranar Asabar, inda suka rika harbi sama domin tsoratar da mazauna yankin kafin su tafi da basaraken da matarsa da kuma mutum daya

Rahotanni na cewa kawo yanzu ba a san inda akai basaraken da sauran mutanen ba, amma hukumomin tsaro na ci gaba da gudanar da bincike kan lamari.

Karin bayani na tafe.

Post masu alaƙa

Gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad Ya ce suna nema Jam’iyyar da za su shiga amma banda APC

Tsohon shugaban hukumar kwallon kafa ta Najeriya Galadima ya rasu

Hadejia ta cika shekaru 120 da cin nasara kan turawan mulkin mallaka na Birtaniya.