Babban Labari

Dubun masu ƙera muggan makamai a Filato ta cika

Dubun wasu masu ƙera muggan makamai ta cika a yankin Lantang da ke Jihar Filato mai yawan fama da rikice-rikice da hare-hare. Sojojin Rundunar Operation Enduring Peace sun kama manyan bindigogi uku, ƙirar AK-47 guda biyu da kuma ƙirar G3 guda ɗaya a hannun masu ƙera makamai ba bisa ka’ida ba. Mutanen sun shiga hannun […]

Read more

Dalilin da ya sa zan yi takara – Yusuf Buhari

Ɗan tsohon shugaban Najeriya, marigayi Muhammadu Buhari, Yusuf Buhari ya bayyana cewa, ya amsa kiran al’ummar mazaɓarsa ne na tsayawa takarar kujerar Majalisar Wakilai. Ya ce, burinsa shi ne ya ɗora kan kishin ƙasa da jajircewar mahaifinsa wajen gina mazaɓarsa, jihar Katsina da ma ƙasa baki ɗaya. Yayin da yake jawabi a Daura bayan wani […]

Read more

An tsinci gawar matashi a kusa Asibitin Mallam Aminu Kano.

An tsinci gawar wani matashi mai suna, Aliyu Mustapha, a cikin Kwalabatin kusa da asibitin Mallam Aminu Kano. Mijin ƙanwar mahaifiyar marigayin, Malam Salisu, ya bayyana cewa makonni biyu kenan suke nemansa amma basu ganshi ba,inda lamarin ya tayar mu su da hankali. Sai dai ya ce daman bashi da lafiya zazzaɓi ne yake damunsa, […]

Read more

Tinubu ya cire ministan kuɗi da na gidaje

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya yi wasu sauye-sauye a majalisar ministocin ƙasar, inda ya cire ministan kuɗi, Wale Edun da ministan gidaje, Ahmed Musa Dangiwa. A wata sanarwa da sakataren gwamnatin ƙasar, Sanata George Akume ya fitar, ya ce an buƙaci ministan kuɗin ya miƙa aiki ga ƙaramin ministan kuɗin ƙasar, Taiwo Oyedele, wanda zai […]

Read more