Babban Labari

Yan bindiga sun sace shugaban ƙaramar hukuma a Zamfara

Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun sace Shugaban Ƙaramar Hukumar Bungudu ta Jihar Zamfara, Alhaji Nura Umar Bungudu, bayan sun kai hari gidansa cikin dare a ranar Alhamis. Rahotanni sun ce maharan sun kawo harin ne har cikin garin Bungudu, inda suka nufi gidan shugaban ƙaramar hukumar da ke unguwar Zango, kusa da […]

Read more

Yar Najeriya ta kammala jami’ar Burtaniya da daraja ta daya (1st Class) a ilimin kimiyar samar da manhajar kasuwancin zamani.

Yar Najeriya, Zainab Muhammad Babandede, ta sake ɗaga martabar ƙasarta, inda ta kammala karatun digirin farko (BSc) a fannin Kimiyyar Samar Da Manhajar Kasuwancin Zamani (Engineering Software for Business) da matsayin Daraja ta Farko (First Class) a Jami’ar University of the West of England (UWE), Bristol, da ke Birtaniya. Wannan gagarumar nasara ta ƙara tabbatar […]

Read more

Dakarun yan sanda 200 sun samu horon sarrafa makami a Kano.

Rundunar yan sandan jihar Kano, karkashin jagorancin kwamishina, CP Ibrahim Adamu Bakori, ta kammala horas da jami’ai 200 kan dabarun sarrafa makami domin ƙara musu ƙwarewa wajen gudanar da ayyukan tsaro. Horon na tsawon wata guda, wanda aka gudanar a sansanonin rundunar yan sandan kwantar da tarzoma ta lamba 9 da ke Hotoro da ta […]

Read more

DSS ta kama waɗanda ake zargi da sace Farfesa A Nasarawa

Hukumar tsaro ta farin kaya ta Najeriya, DSS, ta ceto shugaban sashin tsangayar Noma ta Jami’ar jihar Nasarawa da ke Keffi, Farfesa Samuel Okunsebor, bayan da wasu yan bindiga sun yi garkuwa da shi. Rahotanni sun ce an sace Farfesan ne ranar Laraba a tsakanin ƙananan hukumomin Lafia da Nasarawa Eggon dake Jihar. Jami’an DSS […]

Read more

An gurfanar da waɗanda ake zargi da sace ɗaliban Oyo

Gwamnatin Najeriya ta gurfanar da wasu mutum uku a gaban babbar kotun Ttarayya bisa zarginsu da hannu a sace ɗalibai da malamai daga wasu makarantu a ƙaramar hukumar Oriire ta jihar Oyo. Waɗanda ake zargin sun haɗa da Abdulrazak Umar, wanda aka fi sani da Abu Khalifa ko Abu Khalid, Yunusa Musa, wanda aka fi […]

Read more