Home » An Rantsar Da Tchiani Shugaban Riƙo Na Nijar Na Shekaru 5

An Rantsar Da Tchiani Shugaban Riƙo Na Nijar Na Shekaru 5

An Rantsar Da Abdouramane Tchiani A Matsayin Shugaban Riko Na Jamhuriyar Nijar

by Mujahid Wada Guringawa
0 comment
Ƙasashen Mali da Burkina Faso da kuma Guinea, sun bayyana cewa duk wani yunƙurin yin amfani da ƙarfin soja don dawo da zaɓaɓɓen shugaban ƙasar Nijar Mohamed Bazoum tamkar ƙaddamar da yaƙi ne a kansu.

 

An rantsar da Janar Abdouramane Tchiani a matsayin shugaban riƙo na Jamhuriyar Nijar, wanda zai kwashe shekara biyar yana jan ragamar gwamnati kafin miƙa mulki.

Hakan wani ɓangare ne na aiwatar da rahoton babban taron ƙasar da aka yi a watan Fabairun da ya gabata.

A lokacin shan rantsuwar a ranar Laraba, Tchiani ya kuma zama janar ɗin soja mai tauraro biyar, wanda hakan na daga cikin shawarar taron ƙasar.

Bikin rantsarwar da aka yi a babban ɗakin taro da ke birnin Yamai ya samu halartar sojoji da kuma manyan masu ruwa da tsaki a ƙasar.

Kafin shan rantsuwar na yau, janar Tchiani ya kasance shugaban majalisar ceton ƙasa, wadda aka kafa tun bayan kifar da gwamnatin Muhammed Bazoum.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?