Home » Mutane 886 Ake Zaton Sun Kamu Da Kwalara A Najeriya – NCDC

Mutane 886 Ake Zaton Sun Kamu Da Kwalara A Najeriya – NCDC

by Mujahid Wada Guringawa
0 comment

 

Hukumar yaƙi da cututtuka masu yaɗuwa ta Najeriya, NCDC ta ce kimanin mutane 14 suka rasa rayukansu sakamakon cutar kwalara a tsawon mako biyar, a ƙasar.

Wani rahoton da hukumar ta fitar kan cutar a ranar Talata ya nuna cewa akalla mutane 886 aka yi tunanin sun kamu da cutar a tsakanin 27 ga watan Janairun shekarar 2025 zuwa biyu ga watan Fabairun da ya gabata.

 

Rahoton ya ƙara da cewa an samu ɓullar cutar a jihohi 22 na ƙasar, lamarin da ya shafi ƙananan hukumomi 44.

 

Hukumar ta ce jihar Bayelsa da ke kudancin ƙasar, ta bayar da rahoton zaton mutane 695 sun kamu da cutar ta amai da gudawa.

Sai jihar Rivers da ke biye da ita da mutane 54, yayin da jihar Neja da ke tsakiyar ƙasar, ta bayar da rahoton zargin mutane 33 sun kamu da cutar.

A cewar rahoton, jihohin Sokoto, Yobe, Borno, Katsina, Borno da Adamawa na cikin jihohin da aka samu mutum guda kacal da aka yi zaton sun kamu da cutar a tsawon wannan lokaci.

 

Sai dai hukumar ta ce an samu ƙaruwar cutar amai da gudawar a bana, idan aka kwatanta da daidai lokacin a bara, inda aka samu 506.

Hukumar ta bai wa al’umma shawarar shan ruwa mai tsafta, wanke hannu da sabulu, cin abincin da aka dafa sosai da tabbatar da tsaftar muhalli domin kaucewa kamuwa da cutar ta kwalara.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?