Shahararen Malamin Addinin Musulinci Dokta Idris Dutsen Tanshi Ya Rasu

Daga : Safiyanu Haruna Kutama

Fitaccen malamin addinin Islama da ke Jihar Bauchi, Dokta Idris Abdulaziz Dutsen Tanshi ya riga mu gidan Gaskiya.

Makusantan malamin sun tabbatar da rasuwarsa , Inda ya shafe tsawon lokaci Yana karantarwa da kuma harkar kasuwanci.

Malamin ya yi fama da rashin lafiya inda gabanin watan Ramadana ya fita neman magani a ƙasashen Masar da Saudiyya.

Za a yi jana’izarsa da ƙarfe 10 na safiyar Jumu’a a Masallacin Idi na Games Village da ke Jihar Bauchi.

Post masu alaƙa

An kashe mutum saboda Naira 200 a Ogun

Masu ruwa da tsaki na APC a jihar Akwa Ibom sun yi watsi da tsarin tsayar da ɗan takara ta maslaha

Makarantar kurame ta Katsina ta lashe gasar wasannin guragu ta gwamna Radda