Shahararen Malamin Addinin Musulinci Dokta Idris Dutsen Tanshi Ya Rasu

Daga : Safiyanu Haruna Kutama

Fitaccen malamin addinin Islama da ke Jihar Bauchi, Dokta Idris Abdulaziz Dutsen Tanshi ya riga mu gidan Gaskiya.

Makusantan malamin sun tabbatar da rasuwarsa , Inda ya shafe tsawon lokaci Yana karantarwa da kuma harkar kasuwanci.

Malamin ya yi fama da rashin lafiya inda gabanin watan Ramadana ya fita neman magani a ƙasashen Masar da Saudiyya.

Za a yi jana’izarsa da ƙarfe 10 na safiyar Jumu’a a Masallacin Idi na Games Village da ke Jihar Bauchi.

Post masu alaƙa

Ƴan sandan Kano za su ƙara ƙaimi wajen amsa kiran gaggawa – CP Bakori

Masu Garkuwa Da Janar Rabe Na Neman A Sako ’Yan Bindigar Da Ke Hannun Gwamnati

Gwamna Namadi ya dakatar da hadimansa huɗu