• Home  
  • Rundunar Yan Sanda Ta Musanta Labarin Kai Hari Gidan Wike A Jihar Ribas
- Babban Labari

Rundunar Yan Sanda Ta Musanta Labarin Kai Hari Gidan Wike A Jihar Ribas

  Rundunar yan sandan jihar Ribas ta musanta rahotannin dake yawo a shafukan sada zumunta, cewar wasu batagarin sun kai hari gidan ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, tare da banka masa wuta. Tun a ranar Lahadin data gabata rahotannin ke ta yawo a shafukan sada zumuntar cewa an kone gidan kurmus. Sai dai […]

 

Rundunar yan sandan jihar Ribas ta musanta rahotannin dake yawo a shafukan sada zumunta, cewar wasu batagarin sun kai hari gidan ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, tare da banka masa wuta.

Tun a ranar Lahadin data gabata rahotannin ke ta yawo a shafukan sada zumuntar cewa an kone gidan kurmus.

Sai dai cikin wata sanarwa da kakakin rundunar yan sandan jihar Ribas, SP Grace Iringe-Koko, ta fitar a ranar litinin, ta ce labarin da ake yadawa bashi da tushe balle makama don haka jama’a su yi watsayi dashi.

Iringe-Koko, ta kara da cewa an yi hakanne don tayar da hankalin al’umma,a saboda haka ba za su lamunci yi wa wasu kage ba don tunzura jama’a ba .

Rundunar ta ce babu wani labari makancin haka da ya faruwa a jihar , inda ta bukaci al’umma da su yi watsi dashi labari ne na kanzon kurege.

Haka zalika rundunar taja kunnen masu yada labaran karya da su daina,domin duk wanda aka samu da aikata laifin rundunar zata daukin matakin shari’a akansa.

A karshe rundunar ta tabbatarwa da mazauna jihar cewa jami’an yan sandan na iya bakin kokarinsu don wanzar da zaman lafiya a fadin jihar.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000