• Home  
  • Bola Tinubu Ya Yafewa Maryam Sanda Da Aka Samu Da Laifin Halaka Mijinta
- Babban Labari - Labarai

Bola Tinubu Ya Yafewa Maryam Sanda Da Aka Samu Da Laifin Halaka Mijinta

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu yi afuwa ga Maryam Sanda, wadda aka yankewa hukuncin kisa a shekarar 2020 bisa samun ta da laifin halaka mijinta, mai suna Bilyaminu Bello. Mai magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga, ya bayyana a wata sanarwa da ya fitar , inda ya ce matakin ya zo ne bisa shawarar […]

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu yi afuwa ga Maryam Sanda, wadda aka yankewa hukuncin kisa a shekarar 2020 bisa samun ta da laifin halaka mijinta, mai suna Bilyaminu Bello.

Mai magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga, ya bayyana a wata sanarwa da ya fitar , inda ya ce matakin ya zo ne bisa shawarar kwamitin da ke duba batun yafewa ma su laifi a Najeriya.

Maryam Sanda, mai shekaru 37 a duniya , ta shafe shekaru shida a gidan yarin Suleja kafin samun afuwa daga fadar shugaban kasar Nijeriya.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000