Ƙungiyar Miyetti Allah (MACBAN), ta ce an yi asarar shanu sama da 200,000 a Jihar Kaduna sakamakon satar shanu da matsalolin tsaro tun daga watan Janairun 2026.
Shugaban MACBAN na jihar, Alhaji Abdulhamid Musa, ya kuma ce an kashe sama da mambobin ƙungiyar 50 a tsawon wannan lokaci.
Musa, ya bayyana hakan a wani taron manema labarai kan matsalolin tsaro da suka shafi makiyaya da masu kiwon shanu a Kaduna.
Ya ce an samu nasarar ƙwato wasu daga cikin shanun da aka sace a baya-bayan nan, har da wasu da aka gano a Jihar Legas.
Ya ce ana ƙoƙarin mayar da dabbobin ga mamallakansu.
A cewarsa, wasu daga cikin mambobin MACBAN da aka kashe sun rasu ne sakamakon rikicin manoma da kuma hare-haren ’yan bindiga.
Ya ce yankunan da aka fi samun rahotannin asarar dabbobi sun haɗa da Kachia, Chikun, Kagarko, Giwa, Igabi, Jama’a, Kaura, Sanga, Jaba, Kudan, Makarfi, Lere, Zangon-Kataf da Kauru.
Musa, ya ce shanu ba dukiya ce kawai ga makiyaya ba, domin su ne tushen rayuwarsu kuma dukiyar da suke gada iyaye da kakanni.
Ya yi kira ga gwamnatin Kaduna da hukumomin tsaro da su ƙara ƙaimi wajen magance satar shanu da sauran laifukan da ke faruwa a yankunan karkara.
Shugaban MACBAN ya kuma nuna damuwa kan kasuwar dabbobi ta Rijana da ke Kachia, yana mai cewa akwai zargin cewa wasu dabbobin da aka sace na kai su wannan kasuwar.
Ya buƙaci Sojoji, ’Yan Sanda, NSCDC da sauran hukumomin tsaro su ƙarfafa ayyukan leƙen asiri da kai samame a dazukan da ake zargin ’yan bindiga na ɓuya.
Musa, ya kuma nemi gwamnati ta inganta tsaro a hanyoyin da ake bi wajen jigilar dabbobi, tare da samar da tsarin gano dabbobin da aka sace.
Ya buƙaci a kafa kwamiti na musamman domin tantance asarar da makiyaya suka yi da kuma duba yiwuwar tallafa wa waɗanda suka rasa dabbobinsu.
Ya kuma yi kira ga manoma da makiyaya da su ƙara tattaunawa da haɗin kai domin rage rikice-rikice da samar da zaman lafiya a jihar.
Musa, ya ce MACBAN ba ta goyon bayan satar shanu, ’yan bindiga, garkuwa da mutane, kisa ko wani nau’in laifi, ba tare da la’akari da ƙabila, addini ko sana’ar masu aikata laifin ba.
Sai dai ya yi kira da ka da a ɗauki dukkanin makiyaya a matsayin masu aikata laifi saboda ayyukan wasu mutane.
Ya ce MACBAN za ta ci gaba da aiki tare da gwamnati, hukumomin tsaro, manoma da sarakunan gargajiya wajen magance matsalar tsaro.
