• Home  
  • Zan tabbatar da APC ta lashe zabuka masu zuwa ~ Abdullahi Umar Ganduje
- Siyasa

Zan tabbatar da APC ta lashe zabuka masu zuwa ~ Abdullahi Umar Ganduje

Sabon shugaban jami’iyar APC mai mulki, Abdullahi Ganduje, ya ce zai kama aiki ba ji ba gani domin tabbatar da jam’iyyarsa ta yi nasara a zaɓen gwamnan jihohin Kogi da Bayelsa da za a gudanar ranar 11 ga watan Nuwamban 2023.

Sabon shugaban jami'iyar APC mai mulki, Abdullahi Ganduje, ya ce zai kama aiki ba ji ba gani domin tabbatar da jam'iyyarsa ta yi nasara a zaɓen gwamnan jihohin Kogi da Bayelsa da za a gudanar ranar 11 ga watan Nuwamban 2023.

Sabon shugaban jami’iyar APC mai mulki, Abdullahi Ganduje, ya ce zai kama aiki ba ji ba gani domin tabbatar da jam’iyyarsa ta yi nasara a zaɓen gwamnan jihohin Kogi da Bayelsa da za a gudanar ranar 11 ga watan Nuwamban 2023.

Ganduje ya bayyana haka ne a yau Alhamis, lokacin da yake jawabi bayan tabbatar da shi a matsayin shugaban jam’iyyar APC, a wajen taron majalisar zartarwar jam’iyyar da ya gudana a Abuja.

An kuma zaɓi tsohon mai magana da yawun Majalisar Dattijan Najeriya, Ajibola Basiru, ɗan jihar Osun a matsayin sakataren Jam’iyar.

A jawabin nasa, Ganduje ya gode wa Shugaba Bola Tinubu, ya kuma jaddada cewa zai tabbatar da zaman lafiyar a cikin jam’iyar.

Ganduje ya yi alƙawarin yin aiki tuƙuru wajen tabbatar da nasarar jam’iyar a zaɓen gwamnan jihar Kogi da Imo da Bayelsa

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000