• Home  
  • Gwamnatin Kano za ta fara raba wa ɗalibai mata tallafi
- Labarai

Gwamnatin Kano za ta fara raba wa ɗalibai mata tallafi

Gwamnatin Kano ta bayyana cewa ta fara shirin raba Naira dubu ashirin ga dalibai mata dubu arba’in da biyar a matsayin tallafi domin ƙarfafa wa iyaye su riƙa tura ‘ya’yansu makaranta.

Gwamnatin Kano

Gwamnatin Kano ta bayyana cewa ta fara shirin raba Naira dubu ashirin ga dalibai mata dubu arba’in da biyar a matsayin tallafi domin ƙarfafa wa iyaye su riƙa tura ‘ya’yansu makaranta.

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ne ya bayyana hakan a yayin gudanar da bikin ranar samun ‘yancin Najeriya karo na sittin da uku da aka yi a Sani Abacha Stadium.

Ya kuma ce za a dawo da motocin da ke kai yara mata zuwa makaranta tare da dawo da su unguwanninsu.

Sannan gwamnan ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta gina karin makarantu a ƙananan hukumomi 44 da ke jihar nan domin rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta ko da ke yawa a tituna.

A irin wannan yunƙuri ne, gwamnatin ta shirya aikewa da ɗalibai dubu ɗaya da ɗaya ketare domin yin digiri na biyu da suka samu sakamakon mai daraja ta ɗaya a digirinsu na farko.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000