Home » Afirka ta Yamma: Ba za mu sake lamuntar juyin mulkin soji ba ~ Shugaba Tinubu

Afirka ta Yamma: Ba za mu sake lamuntar juyin mulkin soji ba ~ Shugaba Tinubu

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Afirka ta Yamma: Ba za mu sake lamuntar juyin mulkin soji ba ~ Shugaba Tinubu

DAGA: ISMA’IL SULAIMAN SANI

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa ba za su sake yarda da juyin mulki a kasashen Yammacin Afirka ba.

Tinubu ya bayyana haka ne ranar Lahadi jim kadan bayan an zabe shi a matsayin shugaban kungiyar raya tattalin arzikin kasashen Yammacin Afirka ECOWAS mai kasashe mambobi 15.

Shugaban ya ce, Dimokuradiyya na da wahalar gudanarwa amma ita ce tsarin gwamnati mafi kyau,

Ya kara da cewa: “Babu wani a cikinmu da bai yi yakin neman zabe domin ya zama shugaba ba. Ba mu bai wa sojojinmu kudi da zuba jari a kansu da horar da su don su take ‘yancin jama’a ba…Kada mu zauna a Ecowas kamar kyanwar-lami.”

Sabon shugaban na Ecowas ya kuma yi gargadi kan yadda yankin na Yammacin Afirka ke fama da rashin tsaro sakamakon hare-haren ‘yan ta’adda.

Ya bayyana cewa ta’addanci da rashin tsaro suna matukar kawo koma-baya ga ci-gaban yankin.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?