A yayin taron sauraron ra’ayoyin jama’a da ake gudanar a Kano,
Mataimakin Shugaban majalisar dattawa kuma shugaban
kwamitin duba kundin tsarin mulki na 1999, Sanata Barau Jibrin,
ya tabbatar wa ’yan Najeriya cewa aikin gyaran kundin tsarin
mulki da ake gudanarwa ba shi da wata manufa ta ɓoye, kuma
yana gudana ne bisa buƙatun jama’a.
Ya bayyana cewa kwamitin ya riga ya karɓi daruruwan takardu
daga jama’a kan muhimman batutuwa kamar gyaran tsarin zaɓe
da shari’a, ’yancin kan ƙananan hukumomi da tsaro, da shigar da
mata da sarakunan gargajiya cikin tsarin mulki da batutuwan da
ba a samu daidaito a kansu ba a baya.
Mahalarta taron sun haɗa da wakilai daga jihohin Kano, Katsina,
Kaduna, Sokoto, da Jigawa.
Taron dai wanda aka so a yi ti a baya an ɗage shi domin girmama
marigayi Alhaji Aminu Dantata da tsohon Shugaban Ƙasa
Muhammadu Buhari.

