Home » Al’ummar Kasar Mali Sun Fita Rumfunan Zabe Domin Kada Kuri’ar Raba Gardama

Al’ummar Kasar Mali Sun Fita Rumfunan Zabe Domin Kada Kuri’ar Raba Gardama

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Al'ummar Kasar Mali Sun Fita Rumfunan Zabe Domin Kada Kuri'ar Raba Gardama

Al’ummar Mali sun fita rumfunan zabe domin kada kuri’ar raba gardama a kan sabon kundin tsarin mulkin kasar da sojojin suka yi wa gyaran fuska domin mayar da kasar a kan tafarkin mulkin dimukradiyya.

An bude rumfunan zaben da misalin karfe 8 agogon GMT, yayin da ake sa ran samun cikakken sakamako bayan sa’o’i 72.

Sabon kundin tsarin mulkin da al’ummar Mali sama da miliyan 8 ke kada kuri’ar amincewa ko kuma akasin haka shi ne mataki na farko da sojojin ke yi na tsawaita mulkinsu har zuwa shekarar 2024.

Kasar da ke yammacin Afirka ta kwashe shekarun uku tana karkashin ikon sojoji da suka kifar da halastaciyar gwamatin farar hula ta Ibrahim Boubakar Keita a shekarar 2020.

Batu na tsaro na daga cikin manyan kalubalen da kasar ke fama da shi tun bayan barkewar rikicin ‘yan ta’adda da na ‘yan aware a shekarar 2012.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?