Home » Gombe: Rahotanni Sun Nuna Ana Cigaba da Samun Karuwar Masu Yin Tazarar Haihuwa

Gombe: Rahotanni Sun Nuna Ana Cigaba da Samun Karuwar Masu Yin Tazarar Haihuwa

by Hassan Abdu Mai Bulawus
0 comment
Gombe: Rahotanni Sun Nuna Ana Cigaba da Samun Karuwar Masu Yin Tazarar Haihuwa

Hukumar Lafiya a Matakin Farko ta Jihar Gombe, ta bayyana cewa an samu qaruwar sabin masu yin tazarar haihuwa a jihar, da kimanin mutane 28,561 daga watan Janairu zuwa Maris ɗin 2023.

Ko-odinetar sashin tazarar haihuwa a hukumar, Grace Mabudi ce ta bayyana hakan yayin taron rubu’i na biyu na Ƙungiyar ‘ƴan jarida masu aiki da Ƙungiyar The Challenge Initiative (TCI) kan tazarar haihuwa a jihar.

Grace ta ce “Qaruwar bata rasa nasaba da jajircewar da kafofin watsa labarai da qungiyoyin ci gaba suke yi wajen wayar da kan jama’a musamman iyalai kan mahimmancin tazarar haihuwa. Gaskiya kuna qoƙari”.

Sai dai ta yi qira ga ’ya’yan qungiyar su qara himma wajen samar da kayan da ake amfani da su wajen gudanar da wasu hanyoyin na tazarar haihuwa, wanda shi ne babban qalubalen dake fuskantar ayyukan tazarar a jihar.

A cewarta, jihar tana da wadatatun magungunan tazara, amma tana fama da qarancin kayan da ake amfani da su kamar su auduga, da sirinji, da safar hannu, filasta da sauransu, tana mai tabbatar da cewa dole sai da kayayyakin kafin a iya gudanar da wasu nau’o’in na tazarar haihuwa.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?