Home » An Cimma Matsaya Kan Dakatar Da Haska Fina-finai 22 A Kano

An Cimma Matsaya Kan Dakatar Da Haska Fina-finai 22 A Kano

by Mujahid Wada Guringawa
0 comment

Daga: Safiyanu Haruna Kutama

Hukumar tace finafinai ta jihar Kano ta amince da tsawaita wa’adin dakatar da nuna wasu manyan fina-finai masu dogon zango 22.

Tun da farko hukumat ta sanar da dakatar da nuna finafinan ne sakamakon zarginsu da saɓa ƙa’idar hukumar, sannan ta ba masu finafinan mako ɗaya su cika ƙa’idojin hukumar.

Sai dai a wata sanarwa da shugaban Haɗaɗɗiyar Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Najeriya (MOPPAN) reshen jihar Kano, Ado Ahmad Gidan Dabino, ya ce an tattauna, kuma an fara samun mashalah.

“Bayan doguwar tattaunawa da shugaban hukumar, Abba Al-Mustapha da wasu ma’aikatansa da wakilan Kannywood, an samu matsaya a kan:

Hukumar ta yarda ta ƙara mako ɗaya a cigaba da sakin finafinan da suke a layin fitowa don kada masu finafinan su yi asara

Za a sake zama ranar Alhamis domin sake tattaunawa domin a ƙarƙare maganar.

Daga cikin waɗanda suka halarci taron akwai wakilan MOPPAN da Abdul Amart da Nazifi Asnanic da Abubakar Bashir Maishadda da sauransu.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?