Home » An Sake Kama Wani Mai Garkuwa Da Mutane Zai Tafi Hajji A Sokoto

An Sake Kama Wani Mai Garkuwa Da Mutane Zai Tafi Hajji A Sokoto

Hukumomin tsaro sun kuma kama mai garkuwa da mutane a dai-dai lokacin da yake shirin tafiya aikin Hajji a filin sauka da tashin jiragen sama na jihar Sokoto.

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Daga Safiyanu Haruna Kutama

Hukumomin tsaro sun kuma kama mai garkuwa da mutane a dai-dai lokacin da yake shirin tafiya aikin Hajji a filin sauka da tashin jiragen sama na jihar Sokoto.

Jami’an hukumar tsaron farin kaya (DSS) ne suka kama ɗan ta’addan mai suna Sani Galadi, yayin da ake tantance maniyyata domin hawa jirgin zuwa ƙasar Saudiya

An kama shi ne a safiyar ranar Litinin, washegarin da jami’an tsaro suka kama wani ɗan bindiga yana yana shirin hawa mota zuwa filin jirgin sama na Abuja domin zuwa aikin Hajji.

Wani babban jami’in tsaro a Sakkwato ya shaida wa Daily Trust cewa ana yiwa Sani Galadi tambayoyi kuma yana bayar da muhimman bayanai kafin a gurfanar da shi a kotu.

Da aka tambayi jami’in yadda aka yi dan bindigar ya samu tantancewa domin zuwa aikin Hajji, ya ce “sai a tambayi hukumomin da abin ya shafa”.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?