• Home  
  • An Sake Kama Wani Mai Garkuwa Da Mutane Zai Tafi Hajji A Sokoto
- Babban Labari - Labarai

An Sake Kama Wani Mai Garkuwa Da Mutane Zai Tafi Hajji A Sokoto

Hukumomin tsaro sun kuma kama mai garkuwa da mutane a dai-dai lokacin da yake shirin tafiya aikin Hajji a filin sauka da tashin jiragen sama na jihar Sokoto.

Daga Safiyanu Haruna Kutama

Hukumomin tsaro sun kuma kama mai garkuwa da mutane a dai-dai lokacin da yake shirin tafiya aikin Hajji a filin sauka da tashin jiragen sama na jihar Sokoto.

Jami’an hukumar tsaron farin kaya (DSS) ne suka kama ɗan ta’addan mai suna Sani Galadi, yayin da ake tantance maniyyata domin hawa jirgin zuwa ƙasar Saudiya

An kama shi ne a safiyar ranar Litinin, washegarin da jami’an tsaro suka kama wani ɗan bindiga yana yana shirin hawa mota zuwa filin jirgin sama na Abuja domin zuwa aikin Hajji.

Wani babban jami’in tsaro a Sakkwato ya shaida wa Daily Trust cewa ana yiwa Sani Galadi tambayoyi kuma yana bayar da muhimman bayanai kafin a gurfanar da shi a kotu.

Da aka tambayi jami’in yadda aka yi dan bindigar ya samu tantancewa domin zuwa aikin Hajji, ya ce “sai a tambayi hukumomin da abin ya shafa”.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai