• Home  
  • An Ga Watan Azumin Ramadan A Ƙasar Saudiyya
- Babban Labari - Labarai

An Ga Watan Azumin Ramadan A Ƙasar Saudiyya

Kasar Saudiyya ta sanar da ganin jinjirin watan Ramadan na Shekarar 1446 Bayan Hijra a Yau Din nan.

Daga: Safiyanu Haruna Kutama 

Kasar Saudiyya ta sanar da ganin jinjirin watan Ramadan na Shekarar 1446 Bayan Hijra a Yau Din nan.

Tashar voice of Afric VOA ta rawaito, za a fara Azumin bana a kasa mai tsarki daga gobe asabar, a matsayin 1 ga watan Ramadana .

Kafar yada labarai ta Haramain Sharifain dake kasar Saudiyya ce ta Sanar da hakan a Sahihin shafinta na Facebook da X wato Twitter.

Dama dai yau Juma’a ne 29 ga Watan sha’aban Kuma ita ranar da mai alfarma sarkin musulmi ya bada Umarnin a fara duban jinjirin watan duban wata a Nigeria.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai