Home » An Garkame Majami’u 50 Kan Rashin Bin Doka A Kamaru

An Garkame Majami’u 50 Kan Rashin Bin Doka A Kamaru

Hukumomi a Jamhuriyar Kamaru sun kulle coci-coci hamsin da aka gina ba bisa ƙa’ida ba a babban birnin ƙasar Yaounde.

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Hukumomi a Jamhuriyar Kamaru sun kulle majami’u (Coci-coci) hamsin da aka gina ba bisa ƙa’ida ba a babban birnin ƙasar Yaounde.

Rahotanni daga ƙasar Kamaru sun ce ma’aikata daga ma’aikatar tsare-tsare da gudanar da garuruwa ta ƙasar (MINAT) ne suka rufe coci-cocin yayin da suka kai samame kan wuraren ibadan da aka gina ba bisa ƙa’ida ba.

Kamfanin dillacin labarai na Cameroon News Agency ta ambato DPO na Yaounde na biyu, Daouda Ousmanou, da ya jagoranci aikin yana cewa matsalolin da suka fuskanta sun haɗa da gudanar da coci-coci a cikin gidaje da kuma wurare masu hatsarin gaske.

Ya yi kira ga coci-coci su bi doka ko kuma su fuskanci hukuncin da zai biyo bayan rashin bin doka.

Kazalika mako biyu da suka wuce aka ruwaito cewa an rufe coci-coci 188 a ɓangare na IV na Yaounde a ƙarƙashin jagorancin DPO Elvis Akondi Mbahangwen saboda rashin takardun da ake buƙata.

Tun watan jiya ne dai shugaban MINAT, Paul Atanga Nji, ya sanar da shirin rufe coci-cocin bisa ga ƙorafi da ake yi kan hayaniya da zamba da ɗaiɗaita iyali, kamar yadda kafar yada labarai ta TRT Hausa ta ruwaito.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?