Home » An Kai Mahadi Shehu kurkuku

An Kai Mahadi Shehu kurkuku

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Wata Kotu ta ba da umarnin  a tsare  Mahadi Shehu mai sharhi kan al’amuran yau da kullum a gidan yarisaboda wallafa wani bidiyo iƙirarin cewa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sahale wa Faransa kafa sansanin soja a Arewacin Najeriya.

A ƙarshen makon da ya gabata ne dai Hukumar Tsaro ta farin kaya DSS  ta kama Mahadi Shehu a Kaduna, bayan ya wallafa bidiyon da ke iƙirarin cewa Shugaba Tinubu ya bai wa Faransa dama ta kafa sansanin soja.

Bidiyon da aka ce Mahadi ya wallafa daga baya aka goge, an ga wani hafsan sojan Najeriya yana magana da harshen Hausa, da wani sojan ƙasar waje a bayansa.

Mashawarcin Shugaban Ƙasa kan Sha’anin Tsaro Nuhu Ribadu da Ministan Yaɗa Labarai Mohammed Idris sun ƙaryata iƙirarin na Mahadi a matsayin mara tushe, a wani yunkuri na wanke shugaba Tinubu daga zargin.

Binciken da aka gudanar kan bidiyon da Mahadi Shehu ke iƙirarin sojojin Faransa sun je Jihar Borno domin kafa sansanin soji, ba gaskiya ba ne.

A ranar Talata DSS ta gurfanar da Mahadi Shehu a gaban Mai Shari’a Abubakar Lamiɗo na Babbar Kotun Jihar Kaduna, kan zargin taimaka wa ta’ddanci da tayar da hankalin jama’a.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?