Hukumomin Najeriya sun ce an kama wasu mutum bakwai da ake zargi da kasancewa jiga-jigan a ƙungiyoyin Boko-Haram da ISWAP ne.
Ministan cikin gida na ƙasar, Olubunmi Tunji-Ojo ne ya bayyana haka lokacin sanya hannu kan sabuwar dokar shaidar ɗan ƙasa a Abuja.
Mista Tunji-Ojo ya ce an kama mutanen ne a lokacin d asuka dawo naga aikin Hajji na 2026 a filin jirin saman Katsina cikin makon da ya gabata.
Ministan ya ce an kama mutanen ne bayan bibiyar bayanan mutanen da suka tafi aikin hajji a faɗin ƙasar.
Ya ce yanzu haka mutanen bakwai na hannun hukumar tsaro ta DSS wadda take gudanar da bincike kan lamarin.