An kama wasu mutum 7 da ake zargin ƙusoshin Boko-Haram ne a filin jirgin Katsina

Hukumomin Najeriya sun ce an kama wasu mutum bakwai da ake zargi da kasancewa jiga-jigan a ƙungiyoyin Boko-Haram da ISWAP ne.

Ministan cikin gida na ƙasar, Olubunmi Tunji-Ojo ne ya bayyana haka lokacin sanya hannu kan sabuwar dokar shaidar ɗan ƙasa a Abuja.

Mista Tunji-Ojo ya ce an kama mutanen ne a lokacin d asuka dawo naga aikin Hajji na 2026 a filin jirin saman Katsina cikin makon da ya gabata.

Ministan ya ce an kama mutanen ne bayan bibiyar bayanan mutanen da suka tafi aikin hajji a faɗin ƙasar.

Ya ce yanzu haka mutanen bakwai na hannun hukumar tsaro ta DSS wadda take gudanar da bincike kan lamarin.

Post masu alaƙa

KACRAN ya ti watsi da ƙirƙiro ƴansandan jihohi a Najeriya

INEC na shirin cire NDC daga rajistar jam’iyyun siyasa bayan hukuncin kotu

Za a samu katsewar lantarki a Kano da wasu jihohin Arewa ranar Lahadi