An kama wasu mutum 7 da ake zargin ƙusoshin Boko-Haram ne a filin jirgin Katsina

Hukumomin Najeriya sun ce an kama wasu mutum bakwai da ake zargi da kasancewa jiga-jigan a ƙungiyoyin Boko-Haram da ISWAP ne.

Ministan cikin gida na ƙasar, Olubunmi Tunji-Ojo ne ya bayyana haka lokacin sanya hannu kan sabuwar dokar shaidar ɗan ƙasa a Abuja.

Mista Tunji-Ojo ya ce an kama mutanen ne a lokacin d asuka dawo naga aikin Hajji na 2026 a filin jirin saman Katsina cikin makon da ya gabata.

Ministan ya ce an kama mutanen ne bayan bibiyar bayanan mutanen da suka tafi aikin hajji a faɗin ƙasar.

Ya ce yanzu haka mutanen bakwai na hannun hukumar tsaro ta DSS wadda take gudanar da bincike kan lamarin.

Post masu alaƙa

Kwastam ta kama harsasai 3,300 da kayayyakin fasa-ƙwauri a Seme

Jigawa na da ƙarfin samar da sama da kashi 50 cikin 100 na buƙatar shinkafar Najeriya – Shugaban NUJ

Ba na tsoron duk wata barazana daga Gwamnatin Tarayya a yayin zaɓen Osun — Gwamna Adeleke