Home » An kashe shugabannin Miyetti Allah 7 cikin shekara 2

An kashe shugabannin Miyetti Allah 7 cikin shekara 2

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Shugaban Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah (MACBAN) na jihar Kwara, Idrissu Abubakar cikin alhini.

Ƙungiyar Fulani Makiyaya ta Miyetti Allah (MACBAN) ta tabbatar da kisan da aka yi wa shugabanta na jihar Kwara, Idrissu Abubakar cikin alhini.

A ranar Asabar ne wasu ‘ƴan bindiga ɗauke da makamai ne suka auka gidan shugaban ƙungiyar inda suka halaka shi.
Kisan shugaban Miyetti Allah na jihar Kwaran na zuwa ne kusan wata biyu bayan kashe shugaban ƙungiyar na jihar Katsina, Alhaji Sirajo Ahmad Mairana.

Cikin wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar mai ɗauke da sa hannun babban sakatarenta na ƙasa, Bello Aliyu Gotomo, ta yi Allah wadai da kisan da aka yi wa Idrissu Abubakar mai shekara 33.

Sanarwar ta ambato shugaban ƙungiyar na ƙasa, Baba Othman Ngelzarma na cewa an kashe Idrissu Abubakar da mislain ƙarfe 10:00 na daren da ya gabata bayan komawa gida daga sallar Tarawih.

Ƙungiyar ta ce cikin shekara biyu da suka gabata, ‘ƴan bindiga sun kashe shugabanninta bakwai na jihohi da na ƙananan hukumomi.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?