Home » Za A Yi Sabbin Manyan Makarantu 5 A Zaria A 2025 – Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Za A Yi Sabbin Manyan Makarantu 5 A Zaria A 2025 – Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya, Hon. Tajudeen Abbas ya ce mazaɓarsa ta Zariya za ta samu ƙarin manyan makarantu gwamnatin tarayya biyar da na sakandire biyu a kasafin kuɗin 2025.

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya, Hon. Tajudeen Abbas ya ce mazaɓarsa ta Zariya za ta samu ƙarin manyan makarantu gwamnatin tarayya biyar da na sakandire biyu a kasafin kuɗin 2025.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya, NAN ya ruwaito kakakin majalisar na bayyana a haka a lokacin liyafar buɗe-baki da Hon. Tajudeen ya shirya tare da al’ummar mazaɓarsa a ranar Asabar.

Ya ce matakin yunƙuri ne na ƙarfafa kambin Zariya a matsayinta na cibiyar ilimi mai zurfi.

Kakakin Majalisar ya ce sabbin makarantun da mazaɓar tasa za ta samu sun haɗa da Kwalejin Ayyukan Noma ta Tarayya da Makarantar Kula da Kiwon Dabbobi da Baye ta Tarayya da Kwalejin Fasaha ta Tarayya.

Sauran sun haɗa da Cibiyar Horas da Ayyukan Cigaba da Cibiyar Tattara Fasahohi da makarantar Masu Buƙata ta Musamman – wadda ta ƙunshi furamare da sakandire, da kuma Sakandiren gwamnatin Tarayya, kmar yadda NAN ya ruwaito.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?