Wasu ’yan bindiga sun yi garkuwa da ɗan Majalisar Dokokin Jihar Filato, mai wakiltar Mazaɓar Pankshin ta Kudu, Laven Denty Jacob.
A yammacin ranar Litinin aka yi garkuwa da shia gidansa da ke Anguwan Kagji, a Unguwar Dong, a Ƙaramar hukumar Jos ta Arewa.
Wani na kusa da shi ya tabbatar wa manema labarai cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 7:30.
A cewar mai taimaka wa ɗan majalisar, wasu mutane uku ne, da suka rufe fuskokinsu suka kai hari a ƙofar gidansa, a lokacin da suke jiran jami’an tsaronsa su buɗe kofar.
- Bayan Sallar La’asar Za A Yi Jana’izar Sheikh Abdulaziz Al-Sheikh
- Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf Ya Sauyawa Kwamishinan Shari’a Ma’aikata
Ya bayyana cewa maharan sun ɗauke ɗan majalisar da ƙarfi daga cikin motarsa zuwa wani wuri, da ba a sani ba.
Ya ce masu garkuwar sun buqaci iyalansa su a biya su, kuɗin fansa naira miliyan hamsin.
Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, DSP Alabo Alfred da Shugabannin Majalisar Jihar, har yanzu ba su ce komai ba, kan wannan al’amari.

