An Yi Jana’izar Dokta Idris Dutsen Tanshi

Daga Safiyanu Haruna Kutama

Dubban Mutane daga sassan Najeriya ne suka Halarci Jana’izar Shaik Abdul’aziz Idris Dutsen Tanshi wanda Allah ya yi wa rasuwa a daren  Juma’a.

An gudanar da Jana’izar ne a Masallacin idi na Game Village dake garin Bauchi.

Shaik Abdul’aziz Idris Dutsen Tanshi dai ya rasu yana da Shekaru 68.

ya bar ‘ya’ya 38 da jikoki da Dama Kuma matan sa 3.

Manyan Yan siyasa irin su tsohon matemakin shugaban Nigeriya Atiku Abubakar da kungiyar Jama’atul Izalatul Bidi’a Wa’iqamatus Sunna JIBWIS da sauran manyan malamai tuni suka fara aikewa da sakon ta’aziyya tare da alhinin rasuwar sa.

Post masu alaƙa

AIG Garba Ahmed ya bukaci daliban Sakandaren ’Yan Sanda Dawakin Kudu su zama jakadu na gari.

Babu ɗaga ƙafa tsakanin mu da masu sha da dillancin miyagun ƙwayoyi a Kano – Anti-Phone Snatching Force.

Kwamitin yaki da shaye-shaye da fadan daba na Kano ya nemi hadin kan hukumomin tsaro