• Home  
  • An Yi Wa Gwamnatin Kano Alqunut Kan Zargin Ƙwace Gonaki
- Babban Labari - Labarai

An Yi Wa Gwamnatin Kano Alqunut Kan Zargin Ƙwace Gonaki

Al’ummar garin Gano dake karamar hukumar Dawakin Kudu, sun yi wa gwamnatin Kano Al-Qunut, kan zargin ta da yunkurin kwace musu Gonaki.

Daga: Safiyanu Haruna Kutama

Al’ummar garin Gano dake karamar hukumar Dawakin Kudu, sun yi wa gwamnatin Kano Al-Qunut, kan zargin ta da yunkurin kwace musu Gonaki.

Mutanen sun gudanar da Sallah tare da yin addu’o’in neman dauki daga Ubangiji.

Magidanta, maza da mata hadi da samari ne suka halarci taron addu’ar daya gudana a safiyar yau Litinin.

Mutanen sun ce gwamnatin tana son kwace musu gonakin da girman su yakai kilomita 5 don yin aiki a wajen. Haka ne yasa al’ummar rokon gwamnatin tayi hakuri ta bar musu filayen su.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000