Home » “Ba Rashin Ƙokari Yasa Aka Sauke Ni Daga Minista Ba” -T Gwarzo

“Ba Rashin Ƙokari Yasa Aka Sauke Ni Daga Minista Ba” -T Gwarzo

by Mubarak Ibrahim Mandawari
0 comment

Tsohon Ƙaramin Ministan Gidaje da ƙawata Birane Abdullahi Tijjani Muhammad Gwarzo ya bayyana cewa tun kafin a sauke shi shugaba Tinubu ya sanar dashi.

Tohon ministan ya ƙara da cewa cire shi ko kusa ko alama bashi da alaƙa da rashin ƙoƙari.

T Gwarzo ya ƙara da cewa Tinubu ya sanar dashi suna buƙatar samun wani Ministan daga yankin Kano ta tsakiya.

“Na yi ƙokarin ba da shawara ga lamarin amma dai abun bai yiwu ba, amma cire ni bashi da alaka da rashin ƙoƙari” a cewar tsohon mataimakin gwamnan.

T Gwarzo dai na daga cikin ministocin da shugaba Tinubu ya sauke, duk da ana ganin yana daga cikin makusantan shugaban ƙasar ta fannin siyasa, inda ya maye gurbin sa da  Abdullahi Yusuf Ata shine daga yankin Kano ta tsakiya.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?