Home » Bam Ya Tashi Da Manomi A Neja

Bam Ya Tashi Da Manomi A Neja

by Muhammad Auwal Suleiman

Wani abu da ake zargin bam ne ya tashi da wani manomi mai suna Isyaku Gambo, a kusa da garin Bassa, da ke Ƙaramar Hukumar Shiroro ta Jihar Neja.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne yayin da manomin ke kan hanyarsa ta kai kayan amfanin gona zuwa Bassa.

Kawo yanzu Ana zargin cewa ’yan ta’adda ne suka dasa bam ɗin a kan hanya tsakanin Unguwan-Usman da Bassa.

Wani mazaunin yankin, ya bayyanawa jaridar Aminiya cewa fashewar bam ɗin ta tarwatsa gawar mamacin gaba ɗaya nan take.

“Lamarin ya faru ne a yau (Asabar) da misalin ƙarfe 3 na rana.

“Mamacin na kan hanyarsa ta dawowa daga gona bayan ya ɗauko kayan amfanin gona.

“Wannan ne karo na farko da muka fuskanci irin wannan a nan. Ana zargin ’yan ta’adda ne suka dasa bam ɗin,” in ji wani mazaunin yankin.

Ƙoƙarin samun ƙarin bayani daga kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya ci tura domin bai amsa kiran waya baya.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?

Adblock Detected

Please support us by disabling your AdBlocker extension from your browsers for our website.