Home » Bam Ya Sake Tashi A Zamfara Cikin Sati Guda A Karo Na 3

Bam Ya Sake Tashi A Zamfara Cikin Sati Guda A Karo Na 3

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Wasu bama-bamai guda biyu sun tashi a wasu wurare a gundumar Dansadau da ke karamar hukumar Maru ta jihar Zamfara.

Jaridar PremiumTimes ta ruwaito cewa, bama-baman biyu sun fashe ne akan titin Dansadau zuwa Malamawa dayan kuma a kan titin Malele, duk a gundumar Dansadau.

Wani mazaunin yankin da abin ya faru Nuhu Babangida ya ce wata motar fasinja ce da ke kan hanyar kasuwar mako-mako ta Dansadau a safiyar Juma’a ta taka bam din.

Babangida ya ce bama-baman da suka fashe a kan titin Malamawa da Malele sun tashi ne a lokaci guda amma ba a samu asarar rai ba.

Wannan dai shine karo na uku da bam ya tashi a jihar Zamfara, kuma an dora alhakin tada bama-baman akan ‘yan ta’addar lakurawa.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?