Home » An Sace Motar Malam Nuhu Ribadu

An Sace Motar Malam Nuhu Ribadu

by Mujahid Wada Guringawa
0 comment

Wasu da ake zargin ɓarayi ne sun sace motar ofishin Malam Nuhu Ribadu, mai bai wa shugaban ƙasa shawara a fannin tsaro a wani masallacin juma’a dake birnin tarayya Abuja.

Rahotanni sun bayyana cewa an ajiye motar a kusa da wani masallacin birnin tarayya Abuja da misalin ƙarfe 1:05, lokacin da jami’an ofishin Nuhu Ribadu suka je yin sallar juma’a.

Tuni dai jami’an rundunar ƴan sandan Abuja suka fara gudanar da binciken wadanda suka sace motar mai ƙirar Toyota Hilux.

Rahotanni sun bayyana cewa  jami’an ofishin na Ribadu sun iske babu motar a wajen da suka ajiye ta yayin da suka kammala Sallar Juma’ar

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?