BUA ya tallafa wa ɗaliban Sakoto 200 da miliyan 40

Kamfanin samar da siminti na BUA ya bayar da tallafin karatu Naira miliyan 40 ga ɗalibai 200 da ke manyan makarantu a jihohin tsohuwar Jihar Sakkwato.

An bayar da tallafin domin ganin sun cimma burinsu a fannin ilmi.

Ɗaliban da suka ci gajiyar sun haɗa da matasa 50 daga Sakkwato, 50 daga Kebbi da 50 daga Zamfara, sai 50 a Wamakko inda cibiyar kamfanin simintin yake.

Kowane ɗalibi zai karɓi Naira dubu 200, an samu ninkin ɗaliban kuɗin ma an samu ƙari da kashi 100 bisa ga shekarun baya.

Shugaba kuma Daraktan kamfanin, Injiniya Yusuf Binji ya ce sun ninka yawan ɗalibai daga 100 zuwa 200 haka kuɗin daga dubu 100 zuwa 200.

Injiniya Binji ya bayyana tallafin karatun matsayin saka jari ne da zai samar da al’ummar mai ɗorawa a gaba.

Ya yi kira ga waɗanda suka ci gajiyar su yi abin da ya dace kuma kamfani zai bibiyi karatunsu.

Shugaban Kamfanin na BUA ya gode wa gwamnatin jiha kan samar musu filin kasuwanci ba tsangwama.

Mai baiwa Gwamanan Sakkwato shawara, Honarabul Usman Arzika Fako ya ce tallafin zai bunƙasa ilmi da samar da aikin yi ga matasa.

Ya yaba wa kamfanin ga wannan hoɓɓasar, akwai buƙatar a duba wasu ɓangarori suma a yi abin da ya kamata.

Balkisu Bello Muhammad, ɗaliba daga Kebbi ta bayyana BUA ginshiƙi ne na samar da cigaba ta gode wa kamfanin kan wannan saka jarin da suka yi da za su ci gajiyarsa a gaba.

Umar Bello ɗalibi daga Zamfara ya nuna farin cikinsa ga kamfanin yadda ya ɗaga karatunsa zai samu nasara a gaba.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *