Ba Sulhu Tsakaninmu Da ECOWAS – Nijar, Mali da Burkina Faso
Shugabannin Ƙasashen Mali, Nijar da Burkina Faso, sun sake tabbatar da matsayarsu na ficewa daga Ƙungiyar Raya Tattalin Arziƙin Ƙasashen yammacin Afrika (ECOWAS).
Shugabannin Ƙasashen Mali, Nijar da Burkina Faso, sun sake tabbatar da matsayarsu na ficewa daga Ƙungiyar Raya Tattalin Arziƙin Ƙasashen yammacin Afrika (ECOWAS).
Hukumar Lafiya Ta Duniya (WHO) ta bayyana cewa kaso 30 na masu mutuwa sakamakon zazzabin cizon sauro a duniya ‘yan Najeriya ne.
Hukumar kula da ilimi, kimiya da al’adu ta Majalisar Dinkin Duniya (UNESCO) ta ce a shekarar 2024 an kashe ‘yan jarida 68 a bakin aiki.
Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya sauke sakataran gwanatin jihar Dokta Abdullahi Baffa Bichi da shugaban ma’aikatan fadar gwamnatin jihar Shehu Wada Sagagi an kuma sauke kwamishinoni 5. Wannan na ƙunshe a cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun daractan yaɗa labaran gwamnan na Kano Sunusi Bature Dawakin Tofa. Baya ga haka gwamnan […]
Ukashatu Lawan Diza wani mai laurar gani (makanta) ya bayyana mana cewa a yanzu halin da ake ciki a Najeriya masu bukata ta musamman sun fi sauran jama’a kamuwa da cutar damuwa.
Tsohon gwamnan jihar Sakkwato Attahiru Bafarwa da kuma fitacciyar ‘ƴar gwagwarmaya a Arewacin Najeriya, Hajiya Naja’atu Muhammad, sun ƙaddamar da wata sabuwar tafiyar matasa don ceto yankin Arewacin Najeriya me suna Northern Star Youth Movement Initiative (NSYMI). A jawabinsa, Bafarawa wanda tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa ne a ƙarƙashin jam’iyyar PDP, ya ce, lokaci ya […]
Wani bincike da jaridar Vanguard ta yi ya tabbatar da cewa malaman jami’o’i a Najeriya na cikin kuncin fatara da talauci sakamakon tsadar rayuwar da ake fama da ita a fadin kasar.
Gwamantin Jihar Adamawa ta tabbatar da ta ƙwace ikon naɗa wa da tsige sarakuna daga hannun Lamiɗon Adamawa, Alhaji Mustapha Barkinɗo ta damƙa wa Gwamnan Jihar.
Wani mai sharar asibiti a Kano da ake kira Malam Aminu Umar Kofar Mazugal ya mayar da kudin da ya tsinta da suka kai kimanin Naira miliya 40 ga mai su.
Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya kai ziyara jami’ar Near East da ke kasar Cyprus domin jin dalilin hana ɗaliban da gwamnatin jihar ta ɗauki nauyinsu takardun kammala karatun su.