Labarai

Nentawe Yilwatda Ya Zama Sabon Shugaban APC

Kwamitin zartarwa na Jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya, ya amince da nadin Farfesa Nentawe Yilwalda daga jihar Filato a matsayin sabon shugaban jam’iyyar na ƙasa. An cimma matsayar ne yayin taron kwamitin zartarwar na kasa da ya gudana a Abuja. Taron wanda ke gudana a fadar shugaban ƙasar, ya samu halartar Shugaba Bola Tinubu […]

Read more

Sojoji Sun Halaka Yan Bindiga 95 Tare Da Ceto Mutane 138 A Neja

Dakarun Sojin Najeriya sun kashe gomman ’yan ta’adda a Ƙananan Hukumomin Rijau da Mariga a Jihar Neja. ’Yan ta’addan sun fito ne daga Jihar Zamfara, yayin da suke tafiya a kan babura ɗauke da muggan makamai. Sojoji tare da taimakon jiragen yaƙi na sama sun kai farmaki bayan samun bayanan sirri. Aƙalla ’yan ta’adda 95 […]

Read more

NAFDAC Ta Gano Sinadaran Haɗa Abubuwan Fashewa A Kano

Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta ƙasa (NAFDAC) ta gano wani babban gidan ajiya a Kano da ke cike da sinadarai masu haɗari da ake amfani da su wajen haɗa abubuwa masu fashewa, ciki har da sinadarin sulphuric da nitric acid kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito. Hukumar ta kuma rufe wurin nan […]

Read more

Jami’ar Yusuf Maitama Sule Zata Karrama Aminu Dantata, Ahmad Bamba, Rabi’u Kwankwaso Da Wasu Fitattun Mutane

Shugaban Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta Jihar Kano, Farfesa Mukhtar Atiku Kurawa, ya bayyana cewa jami’ar ta yanke shawarar karrama marigayi Sheikh Ahmad Bamba sakamakon gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban jami’ar tun kafin rasuwarsa. Farfesa Kurawa ya bayyana hakan ne a wata zantawa da ya yi da manema labarai, inda ya ce wannan […]

Read more

Hisbah Ta Lalata Barasa Ta Naira Miliyan 5.8 A Jigawa

Hukumar Hisbah ta ce ta kama tare da lalata barasa da ta kai kimanin naira miliyan 5.8 a karamar hukumar Kazaure ta Jihar Jigawa. Kwamandan Hisbah a jihar Malam Ibrahim Dahiru ne ya bayyana haka a wata hira da manema labarai a Dutse, babban birnin jihar. Ya ce an gudanar da aikin ne karkashin jagorancin […]

Read more

Tinubu Zai Karɓo Rancen $21bn Daga Ketare

Majalisar Dattawa ta amince da buƙatar Shugaba Bola Tinubu ta karɓo bashin ƙasashen waje da ya haura dala biliyan 21 domin aiwatarwa da cike giɓin kasafin kuɗin shekarar 2025 zuwa 2026. Majalisar ta bayyana cewa za a yi amfani da bashin ne wajen aiwatar da muhimman ayyukan ci gaban ƙasa, musamman a fannonin ababen more […]

Read more