Kungiyar Likitocin Nijeriya Ce Zata Tantance Sahihancin Rashin Lafiyar Nnamdi Kadu: Kotu

Babban Kotun Tarayya ta daƙile buƙatar Nnamdi Kanu na neman a kai shi asibiti, inda ta umarci shugaban ƙungiyar likitocin Najeriya (NMA) ya kafa kwamitin likitoci tsakanin takwas zuwa goma domin tantance lafiyar shugaban ƙungiyar IPOB da ya ke ikirarin fama da rashin lafiya mai tsanani.

Mai shari’a James Omotosho ne ya bayar da wannan umarni yayin da ya ke yanke hukunci kan buƙatar da Kanu ya shigar, inda ya nemi a mayar da shi ɗakin kulawa na musamman a asibitin ƙasa saboda yana fama da rashin lafiya mai tsanani.

Alƙalin ya ce kwamitin da NMA za ta kafa zai binciki ainihin matsalar lafiyar Kanu domin gano ko hakan na iya hana shi ci gaba da fuskantar shari’a.

Haka kuma, kwamitin zai duba ingancin cibiyar kiwon lafiya ta Hukumar Tsaro ta DSS, domin tabbatar da ko za su iya kula da lafiyar wanda ake tuhuma yadda ya kamata.

Omotosho ya kuma ƙara da cewa kwamitin zai tantance ko akwai buƙatar kai Kanu asibitin ƙasa kamar yadda ya nema, da kuma ko matsalolin lafiyar sa za su iya hana shi tsayawa gaban kotu.

Haka zalika, kotun ta umurci babban daraktan asibitin ƙasa ko wakilinsa ya kasance cikin wannan kwamitin.

Ya kuma uarci shugaba da sakataren kwamitin su saka hannu kan rahoton binciken sannan a mika shi ga kotu cikin kwanaki takwas daga yau (26 ga Satumba, 2025).

Post masu alaƙa

Ƙungiyar muhaɗu mugyara ta bayyana Muhasa TVR a matsayin kan gaba wajen gyaran tarbiyyar al’umma.

Fursuna ya tsere bayan hatsarin motar jami’ai a Yobe

Katsina ta kafa kotunan tafi da gidan ka don gaggauta hukunta ’yan ta’adda