Wani Mutum Ya Zuba Shinkafar Bera A Abincin Da Ya Ci A Kano

Wani mutum ya zubawa abincinsa shinkafar Bera, akan Titin Audu Bako Way Dake Jihar Kano.

Ana Zargin mutumin ya zuba gubar ce bayan ya sayi Wata shinkafa da miya kuma Sai da ya fara ci sannan ya nunawa mutane abunda ya zuba cikin abincin.

Shaidun gani da ido sun tabbatar da cewa, ya shiga gidan abinci ne ya siyo sannan ya zuba gubar kafin ya ci.

Yanzu haka an garzaya da shi zuwa Asbitin Nassarawa don bashi kulawar gaggawa sakamakon faduwa da ya yi kuma baya cikin haiyacinsa.

Post masu alaƙa

Ƴan sanda sun fara bincike kan mutuwar wanda ake zargi da sokawa matashi Wuƙa a Kano

Babachir Lawal ya fita daga ADC

DSS ta kama mutane 5 da ake zargi da sace ɗaliban makarantar St. Mary’s Pipiri a jihar Neja