Home » Dan majalisa Jibrin Ismail Falgore, ya zama shugaban majalisar dokoki ta jihar Kano

Dan majalisa Jibrin Ismail Falgore, ya zama shugaban majalisar dokoki ta jihar Kano

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Dan majalisa Jibrin Ismail Falgore, ya zama shugaban majalisar dokoki ta jihar Kano
Zaɓaɓɓen ɗan majalisa mai wakiltar ƙaramar hukumar Rogo, Jibrin Ismail Falgore, ya zama shugaban majalisar dokoki ta jihar Kano karo ta 10.

Falgore ya yi nasarar zama shugaban majalisar ne ba hamayya bayan da dan majalisar Dala na jam’iyyar NNPP ne ya ayyana falgore a matsayin wanda yake ganin dacewarsa wajen shugabantar majalisar.

Nan da nan ɗan majalisa mai wakiltar ƙaramar hukumar Takai, Musa Ali Kachako, daga jam’iyyar APC ya mara masa baya.

Sannan kuma dan majalisa mai wakiltar Rimingado da Tofa Muhammad Bello Butubutu daga jam’iyyar NNPP ya yi nasarar zama mataimakin majalisar dokokin ta jihar Kano.

Shi ma ya haye wannan kujera ne batare da hamayya ba bayan Zubairu Hamza Masu mai wakiltar Sumaila daga jam’iyyar NNPP ya ayyana shi a matsayin wanda ya dace da zama mataimakin Falgore.

Jam’iyyar NNPP ce dai take da rinjayen da yawan ‘yan majalisu 26, sai kuma APC ‘yan majalisu 14.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?