Hukumar tsaro ta farin kaya a Najeriya, DSS ta kama tsohon attoni janar kuma ministan shari’a, Abubakar Malami.
Wata majiya mai tushe daga hukumar ta tabbatar da cewa DSS ɗin ta kama shi ne bisa zargin tallafa wa ta’addanci, bayan gano makamai da harsasai a gidansa da ke birnin Kebbi.
Kazalika, BBC ta zanta da wani makusanci tsohon ministan, Honorable Abubakar B Sabo, tsohon ɗan majalisar Birnin Kebbi, inda shi ma ya tabbatar da kamen.
An kama Malami wanda ake tuhuma a gaban wata babbar kotun tarayya a Abuja kan zargin halasta kuɗin haram, ranar Litinin jim kaɗan bayan sake shi daga gidan yarin Kuje da ke Abuja.
Jami’an gidan gyaran halin sun tabbatar da sakin Malami bayan cika sharuɗan beli.
A ranar 7 ga watan Janairu, Kotun Tarayya da ke Abuja ƙarkashin jagorancin alƙali Emeka Nwite ta amince da bayar da belin tsohon ministan shari’a Abubakar Malami da iyalinsa kan kuɗi naira miliyan 500 da kuma mutum biyu da za su tsaya musu.
A cewar alƙalin, mutanen da za su tsaya musu sai sun kasance suna da filaye a yankunan Asokoro da Maitama ko Gwarinpa, sannan kuma sai sun miƙa dukkan takardun tafiyarsu ga kotu.
