• Home  
  • Gwamnan jihar Sakkwato ya amince da biyan ma’aikata albashin watan Yuni da kudin fansho
- Labarai

Gwamnan jihar Sakkwato ya amince da biyan ma’aikata albashin watan Yuni da kudin fansho

Gwamnan jihar Sokoto Ahmed Aliyu ya amince da biyan albashin watan Yuni nan take ga ma’aikatan jihar da kananan hukumomi da kuma malamai kazalika da yan fansho.

Gwamnan jihar Sakkwato ya amince da biyan ma'aikata albashin watan Yuni da kudin fansho

Gwamnan jihar Sokoto  Ahmed Aliyu ya amince da biyan albashin watan Yuni nan take ga ma’aikatan jihar da kananan hukumomi da kuma malamai kazalika da yan fansho.

Wannan na kunshe ne a wata sanarwa  dauke da  sa hannun mai magana da yawun gwamnan jihar Sokoto Malam Abubakar Bawa

Sanarwar tace wannan yunkurin dai nada manufar ganin ma’aikatan jiha sun samu sukunin gudanar da sallah Babba a cikin walwala.

Gwamnan  ya kara jaddada aniyar gwamnatin sa na ganin ta kyautatawa ma’aikata tare Kuma da farfadowa da darajar aikin gwamnati. Haka kuma, ya bukaci ma’aikatan dasu sakawa wannan yunkurin ta hanyar zamowa masu gaskiya,tsare aiki da kuma zuwa aiki cikin lokaci

Gwamna ahmad Aliyu ya kuma roki alummar jihar Sokoto dasu ci gaba da yiwa Gwamnati addua don samun nasarar biyan bukatun jama’a

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai