Home » Gwamnan Kano ya shawarci al’umma su kwantar da hankalinsu

Gwamnan Kano ya shawarci al’umma su kwantar da hankalinsu

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Gwamna Kano ta shawarci al’umma su kwantar da hankalinsu

Gwamnatin Kano ta shawarci al’umma da su kwantar da hankalinsu kuma su guji yin duk abin da zai iya zama saɓa wa doka.

A yammacin jiya Alhamis, wata majiya ta ce Kwamishinan yada labarai na Kano, Alhaji Baba Halilu Dantiye ya yi wannan kira a wani jawabi da ya fitar, inda ya ce shawarar ta zama dole ne ganin cewa wasu bata-gari za su iya amfani da damar shari’ar zabe, su kawo rikici a Kano.

A cewar kwamishinan, akwai buƙatar a zauna lafiya domin cigaban jihar Kano da kuma daukacin kasa. Daga nan ya yi kira ga jami’an tsaro da su ƙara ƙoƙari wajen ganin sun tabbatar da zaman lafiya da aminci.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?