• Home  
  • Gwamnan Osun Ya Buƙaci Tattaunawa Tsakanin Najeriya Da Amurka
- Babban Labari - Labarai

Gwamnan Osun Ya Buƙaci Tattaunawa Tsakanin Najeriya Da Amurka

Gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke ya yi kiran sabunta tattaunawar diplomasiyya tsakanin Najeriya da Amurka, yayin da ake samun ƙaruwar nuna yatsa tsakanin ƙasashen biyu. Cikin wata sanarwa da kakain gwamnan, Olawale Rasheed ya fita,, Gwamnan Adeleke ya buƙaci a tattauna kan barazanar da Shugaban Amurka ya yi a baya-bayan nan kan kai wa Najeriya […]

Gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke ya yi kiran sabunta tattaunawar diplomasiyya tsakanin Najeriya da Amurka, yayin da ake samun ƙaruwar nuna yatsa tsakanin ƙasashen biyu.

Cikin wata sanarwa da kakain gwamnan, Olawale Rasheed ya fita,, Gwamnan Adeleke ya buƙaci a tattauna kan barazanar da Shugaban Amurka ya yi a baya-bayan nan kan kai wa Najeriya hari.

Trump ya yi barazanar kai wa Najeriya hare-hare sakamakon abin da ya kira yawan kisan kiristoci a ƙasar.

Gwamnan ya yi kira a samar da wata hanyar lalama domin samo bakin zaren tsakanin ƙasashen biyu.

“Ina kira ga fadar shugaban Amurka ta tallafa wa Najeriya wajen aiwatar da sabbin dabarun tsaro na zamani”, in ji shi.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai