Home » Gwamnatin Najeriya ta sake kwaso ‘yan Kasarta 126 daga kasar Sudan saboda rikicin yaki

Gwamnatin Najeriya ta sake kwaso ‘yan Kasarta 126 daga kasar Sudan saboda rikicin yaki

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Gwamnatin Najeriya ta sake kwaso 'yan Kasarta 126 daga kasar Sudan saboda rikicin yaki

Gwamnatin Tarayya ta sake kwaso ‘yan Nijeriya 126 daga ƙasa Sudan sakamakon rikicin da ake yi a ƙasar tsakanin sojoji da rundunar RSF.

Mutanen da jirgin kamfanin Tarco ya ɗebo sun sauka a filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja da misalin ƙarfe 4:56 na yammacin jiya Asabar.

Hukumar agajin gaggawa ta Najeriya, NEMA, ita ce ta jagoranci ɗebo mutanen tare da haɗin gwiwar ma’aikatun harkokin waje da ta ‘yan Najeriya mazauna ƙetare, da sauransu.

Sai dai har yanzu akwai ɗaruruwan ‘yan Najeriyar da ke roƙon a kwaso su daga Sudan ɗin amma babu tabbas ko gwamnatin ƙasar za ta ci gaba da aikin kwashe su a yanzu.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?