Home » Wasu tsuntsaye masu Jan baki sun afkawa gonakin noman shinkafa a jihar Kebbi

Wasu tsuntsaye masu Jan baki sun afkawa gonakin noman shinkafa a jihar Kebbi

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Wasu tsuntsaye masu Jan baki sun afkawa gonakin noman shinkafa a jihar Kebbi

Aƙalla mutum 100 ne suka rasa gonakinsu yayin da dandazon tsuntsaye jan-baki suka afka wa gonakin shinkafa a garin Argungu na jihar Kebbi.

Mazauna yankin sun ce tsuntsayen sun lalata kusan hekta 75,000 na gonankin a ranakun ƙarshen makon nan.

Sun ƙara da cewa “Bayan matsalolin da muke ciki na tsadar man fetur da taki, ga kuma tsuntsaye.

Mutum bai isa ya zauna a gida ba, in ba haka ba kuma za su lalata gonarsa baki ɗayanta,” Wani manomin min ma ya ce ya shafe shekara 20 yana noman shinkafa amma bai taɓa ganin irin wannan bala’i ba.

Ba wannan ne karon farko da ake samun hare-haren tsuntsayen ba amma wannan ne mafi muni a baya-bayan nan.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?