Home » Shugaban Kungiyar Kwadago, NLC, Ya Nemi Gwamnatin Tarayya ta Hana Karin Kudin wutar Lantarki

Shugaban Kungiyar Kwadago, NLC, Ya Nemi Gwamnatin Tarayya ta Hana Karin Kudin wutar Lantarki

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Shugaban Kungiyar Kwadago, NLC, Ya Nemi Gwamnatin Tarayya ta Hana Karin Kudin wutar Lantarki

Ƙungiyar ƙwadago ta NLC ta ƙi amincewa da shirin da ake yi na ƙara kuɗin wutar lantarki da kaso 40 ckin 100 nan da 1 ga Yulin 2023.

A sanarwar da ya fitar a Abuja, Kwamared Ajaero ya ce shirin na nuna halin ko-in-kula da rayuwar talakawan Najeriya.

Hukumar kula da farashin lantarki ta ƙasa ce ta amince da ƙarin kuɗin saboda tashin farashin man fetur da kuma karyewar darajar Naira.

Sai dai shugaban na NLC ya buƙaci gwamnati ta hana wannan ƙarin kuɗin wutar.

A cewarsa “dole ne ayi la’akari da adadin wutar da kamfanonin rarraba wutar lantarki ke kawowa da kuma ƙarfin aljihun masu amfani da lantarki wurin biyan kuɗin.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?