• Home  
  • Shugaban Kungiyar Kwadago, NLC, Ya Nemi Gwamnatin Tarayya ta Hana Karin Kudin wutar Lantarki
- Labarai

Shugaban Kungiyar Kwadago, NLC, Ya Nemi Gwamnatin Tarayya ta Hana Karin Kudin wutar Lantarki

Ƙungiyar ƙwadago ta NLC ta ƙi amincewa da shirin da ake yi na ƙara kuɗin wutar lantarki da kaso 40 ckin 100 nan da 1 ga Yulin 2023.

Shugaban Kungiyar Kwadago, NLC, Ya Nemi Gwamnatin Tarayya ta Hana Karin Kudin wutar Lantarki

Ƙungiyar ƙwadago ta NLC ta ƙi amincewa da shirin da ake yi na ƙara kuɗin wutar lantarki da kaso 40 ckin 100 nan da 1 ga Yulin 2023.

A sanarwar da ya fitar a Abuja, Kwamared Ajaero ya ce shirin na nuna halin ko-in-kula da rayuwar talakawan Najeriya.

Hukumar kula da farashin lantarki ta ƙasa ce ta amince da ƙarin kuɗin saboda tashin farashin man fetur da kuma karyewar darajar Naira.

Sai dai shugaban na NLC ya buƙaci gwamnati ta hana wannan ƙarin kuɗin wutar.

A cewarsa “dole ne ayi la’akari da adadin wutar da kamfanonin rarraba wutar lantarki ke kawowa da kuma ƙarfin aljihun masu amfani da lantarki wurin biyan kuɗin.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai