A wani yunkuri na bai wa matasan Najeriya kwarewar sana’o’i da rage rashin aikin yi, tare da inganta harkokin kasuwanci domin cigaban kasa, gwamnatin tarayya ta hannun Ma’aikatar Ilimi ta bude shafin rajista ga masu sha’awar shiga zagaye na biyu na shirin Koyon Fasaha da Sana’o’i (TVET).
Shirin zai bayar da horo na aiki kai tsaye na tsawon watanni 6 ko shekara 1 a cibiyoyi da aka tantance a dukkan jihohi 36 na kasar nan da kuma Babban Birnin Tarayya, Abuja. Kowanne mahalarta zai rika karbar tallafin kudi na ₦22,500 duk wata.
A karshen shirin, za a ba mahalarta takardar shaidar kwarewa da gwamnatin kasa ta amince da ita, bisa cikakken halartar horon.
Horarwar za ta kunshi fannoni masu matukar bukata kamar ICT, gine-gine, noma, fasahar mota, kafafen sadarwa na zamani, sana’ar dinki, kwalliya, yawon bude ido, girke-girke, da sarrafa fata.
Haka kuma, shirin yana hadin gwiwa da Ma’aikatar Fasaha, Al’adu da Yawon Bude Ido ta Tarayya domin fadada damar samun aiki a bangaren kirkira da al’adu.
Domin tabbatar da gaskiya da bin ka’ida, za a rika bibiyar halartar mahalarta ta hanyar tsarin na’urar biometric, kuma biyan tallafi zai danganta da yadda mahalarta ke bin dokokin halarta.
Masu nema dole ne su gabatar da NIN da BVN yayin rajista ta shafin yanar gizo na hukuma.
Masu sha’awa za su iya yin rajista ta wannan shafi:
https://education.gov.ng

